Wani jirgin dakon kaya da Rasha ta kera dauke da wasu fasinjoji ya yi hatsari a ranar 4 ga watan Nuwamba bayan tashinsa daga filin jirgin saman babban birnin Sudan ta Kudu, inda ya kashe mutane akalla 41 da ke cikinsa da wasu a kasa, in ji wani jami'i da wani ganau.
Wani ma'aikacin jirgin da wani yaro da ke cikin jirgin sun tsira da rayukansu, kamar yadda kakakin shugaban kasar Ateny Wek Ateny ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Ya ce mai yiwuwa jirgin na dauke da mutane kusan 20 da suka hada da ma’aikata da fasinjoji 10 zuwa 15, yayin da ba a san adadinsu ba a kasa. Amma ya ce ana ci gaba da tattara lambobi.
Wani dan sanda da bai bayyana sunansa ba, ya ce akalla mutane 41 ne suka mutu. Wani shaida na Reuters ya kuma ce ya ga gawarwaki 41 a wurin.



