Shugaban rundunar sojin Masar ya bayyana kai tsaye ta gidan talabijin inda ya sanar da dakatar da kundin tsarin mulkin kasar.
Janar Abdul Fattah Al-Sisi, wanda yake da shugabanin addini da na soji, ya ce babban alkalin kotun tsarin mulkin kasar ne zai karbi ikon fadar shugaban kasa.
Sanarwar nasa na nufin shugaba Mohammed Morsi ba ya kan mulki.
Masu zanga-zangar adawa da Morsi a dandalin Tahrir na birnin Alkahira sun nuna farin ciki matuka dangane da jawabin.
Matakin dai ya biyo bayan zanga-zangar da aka kwashe kwanaki hudu ana yi na nuna adawa da Mr Morsi a kan tituna, da kuma wa'adin da sojoji suka bayar wanda ya kare a yammacin Laraba.
A halin yanzu dai ba a san inda Mr Morsi yake ba.
BBC



