Firaministan Turkiyya Recep Tayyip Erdogan da ministan harkokin wajen kasar Ahmet Davutoglu za su ziyarci kasar Azabaijan.
Firaministan Turkiyya Recep Tayyip Erdogan da ministan harkokin wajen kasar Ahmet Davutoglu za su ziyarci kasar Azarbaijan domin halartar tarukan kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO.
Sanarwar da Ma'aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar ta ce, Davutoglu zai halarci taron majalisar ministocin ECO karo na 20 da za a yi a Baku a ranar 15 ga watan Oktoba.
A halin yanzu Erdogan da Davutoglu za su halarci taron koli na 12 na shugabannin kasashen ECO da za a yi a ranar 16 ga Oktoba.
(Kamfanin dillancin labarai na Anatolia)


